Kamfanin dillancin labaran iqna, paul Halim ya fadawa manema Labaru cewa; Jami'an tsaron kasar Masar ne su ka gano bom din da aka aje da tazarar mita 20 daga majami'ar da ke yankin Smoutha da garin Alexandria tare kuma da lalata shi.
Kakakin kungiyar Kiristocin na Kibdawa ya kara da cewa; Wasu mutane ne wadana ba a tantance su ba su ka ajiye bom din a kusa da majami'ar
A ranar 5 ga watan nan na Janairu ma dai an dasa wani bom a cikin majami'ar da ke gabacin birnin alqahira wanda kuma ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda da jikkata wasu uku
Da akwai kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar ta Masar wadanda suke yawaita kai hare-hare mabiya addinin kirista da majami'oinsu.
3780248