Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa a jiya kwamitin tsaron maalisar dinkin duniya ya gudanar da wani zama na musamman kan batun halin da ake ciki a Palastine.
Rahoton ya ce wannan zama ya hada dukkanin mambobin kwamitin su goma sha biyar, inda suka tattauna kan abubuwan da suka wakna baya-bayan nan a tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da kuma Faastinwa.
Daga cikin abubuwan da zaman ya yi dubia kansu akwai jerin gwanon da ake gudanarwa akowace juma’aa cikin yankin zirin Gaza da kuma irin matakan da Isra’ila take dauka na yin kisan gilla a kan fararren hula masu jerin gwanon na lumana.
Duk da cewa Amurka taki amincewa da kuduror da dama da ake dauka domin takawa Isra’ila urki kan irin wadannan matakai da take dauka, amma saura mambobin kwaitin suna goyon bayan dakatar da Isra’ila daga kisan kiyashin da take yi wa Falastinawa.