Kamfanin dillancin labaran iqna, bangaren yada labarai na ma'aikatar kula da al'adun muslucni ya sanar da cewa, Shifa Garba daya daga cikin jagororin kungiyoyin mata musulmi a Najeriya da kuma karamin jakadan Iran a kasar Sayyid Mahmud Azimi Nas-Abadi, sun tattauna batun fara gudanar da gasar.
Yanzu haka ana shirin gudanar da gasar kur'ani mai sarki a tarayar Njeriya a birnin Abuja a cikin wannan wata na ramadana mai alfarma.
Bayanin ay ci gaba da cewa, karamin ofishin jakadancin jamhuriyar musulucni ta Iran a birnin an Abuja ne ya shirya daukar nauyin wannan gasa, wadda za ta hada makaranta da mahardata kur'ani mai tsarki daga sassa daban-daban na kasar.
Tarayyar Najeriya wadda ita ce kasa mafi girma a nahiyar Afrika, na daga cikin kasashen da ake mayar da muhimamnci matuka wajen gudanar da ayyuka da suka shafi kur'ani mai tsarki musamamna cikin watan ramadan.
Wannan gasa za ta kasance ne a matakai daban-daban, akwai mataki na hardar kur'ani baki daya, sai kuma masu hardar rabin kur'ani, da kuma amsu rubu'i, bayan an kuma a kwai bangaren tilawa.
bayan kammala gasar wadda za ta dauki 'yan kwanaki ana gudanar da ita, za a bayar da kyautuka ga dukaknin wadanda suka halarci gasar, haka nan kuma za a bayar da wasu kyautukan na musamman ga wadanda suka fi nuna kwazoa yayin gudanar da gasar.