IQNA

Nasrullah Ya Aike Da Sako Jinjina Ga Zarif

22:55 - August 15, 2019
Lambar Labari: 3483950
Bangaren kasa da kasa, Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta Lebanon ya jinjinawa ministan harkokin wajen Iran akan tayin dakansa wajen kalubalantar Amurka

Kamfanin dillancin labaran iqna, a wata wasika da babban kwamandan na kungiyar Hizbullah ya aikewa da ministan harkokin wajen na jamhuriyar musulunci ta Iran, Sayyid Hassan Nasarallah ya ce;

Na rubuto muku wasika ne saboda in bayyana goyo baya da girmamawa a gare ku,saboda shigar da ku cikin jerin sunayen daukaka.

Sayyid Nasarallah yana ishara ne da jerin sunayen mutanen da Amurka take kakabawa takunkumi da a bayan nan ta shigar da sunan ministan harkokin wajen na Iran.

A cikin wasikar, babban sakataren kungiyar ta Hizabullah ya bijiro da yadda yakin kwanaki 33 na 2016 ya kasance ta fuskar diplomaisyya, da yadda sakataren harkokin wajen Amurka ya bukaci a tsagaita wutar yaki.

3835046

 

captcha