IQNA

A Ranar Arafah Za a Sauya Kyallen Dakin ka’abah Mai Alfarma

22:24 - September 29, 2014
Lambar Labari: 1455480
Bangaren kasa da kasa, majiyoyin hukumar kula da ayyukan harami a Saudiyya sun tabbatar da cewa aranar Arafah ne za a gudanar ada aikin canja kyallen da ke kan dakin ka’abah mai alfarma.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo muslim walch cewa, Abdulrahamn Al-sudais shugaban hukumar kula da ayyukan harami a Saudiyya ya tabbatar da cewa a ranar Arafah ne za a gudanar ada aikin canja kyallen da ke kan dakin ka’abah mai alfarma kamar dai yadda aka saba.
Jami’in ya ci gaba da cewa ana yin wannan aiki a kowace shekara a tsawon tarihi, kuma a kan dunka wannan kya;lle a kasar Masar da kuma wasu daga cikin kasashen musulmi, kuma a kan wanke dakin ka’abah da ruwan furanni daga birnin Kashan na kasar Iran, wanda kuma hakan yana daga cikin abin da ake yi tun tsawon daruruwan shekaru.
A kan wannan kyalle dai ana rubuta ayoyin kir’ani mai tsarki nay abo da girmama ga matsayin ubangiji madaukakin sarki, haka nan kuma a kan rubuta sunayen ubangiji masu tsarki a dukkanin bangarori na wannan kyalle, bayan duba shi da kuma tabbatar da cewa dukkanin abubuwan da aka rubuta a kansa da suka hada ayoyin kur’ani da sunayen ubangiji daidai suke ba tare da wani kure ba, to daga nan za a mika shi ga hukumar da ke kula da haramin mai tsarki, wadda it ace za ta sanar da ranar saka a shi a kandakin mai albarka.
1454795

Abubuwan Da Ya Shafa: Kaabah
captcha