Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Masar cewa, Malam Muhammad Abdulwahab Tantawi, Abdulnasir Alhirk, Rafik Naklawi, Umar Diramasi, suna daga cikin fitattun makaranta kur’ani mai tsarki na kasar Masar, kuma dukkaninsu sun hadua cikin wannan shiri wanda gidan radio Zefta da ke cikin jahar Algharbiyya ya shiya.
Muhammad abdulhaq Baha shi ne ya jagoranci gabatar da wannan shiri da ya kayatar da jama’a matuka a wannan gidan radio, haka nan shi ma Ashrafi Fahmi babbanfatawa na kasar shawara shi ma ya kasancea cikin wannn\an shiri.
Malam abdulwahab Tantawi ya gabatar da karatun kur’ani mai tsarki da muryarsa mai dadi, kamar yadda su ma Naklawi da Diramasi sun gudanar wakokin yabo da bege a cikin shirin.