IQNA

The Guardian: Saudiyyah Da Birtaniya Ne Ke Da Alhakin Kisan Al'ummar Yemen

22:47 - December 23, 2016
Lambar Labari: 3481063
Bangaren kasa da kasa, Jaridar The Guardian da ake bugawa a kasar Birtaniya, ta buga wani rahoto da ta harhada dangane da da yakin da Saudiyya take kaddamarwa a kan al'ummar kasar Yemen a fitowarta ta jiya Alhamis.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, A cikin rahoton nata, jaridar ta ce kisan kiyashin da ake yi wa al'ummar kasar Yemen ba aikin kasar Saudiyyah ne ita kadai ba, tana yin hakan ne tare da gwamnatin Birtaniya, domin Birtaniya ce ke sayar wa Saudiyya da mafi yawan makaman da take yin amfani da su wajen aki hare-hare a kan biranan Yemen, da suka hada har da makaman cluster da aka haramta yin amfani da su a duniya.

Jaridar ta ce bai kamata a rufe ido saboda maslaha ta ribar makamai da ake samu a yakin Yemen ba, domin kuwa abin da ake yi kisan fararen hula ne, wanda yake a matsayin laifin yaki, kuma lokaci na zuwa da dukkanin abin da ake yi kullawaa asirce zai bayyana ga kowa a duniya.

3555937


captcha