Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa, Shafin yada labarai na Islamic News na asar Amurka ya bayar da rahoton
cewa, rahotanni da babbar cibiyar musulmin Amurka ta tattara dangane da
hare-haren da aka kai wa masallatan musulmi a fadin kasar ya nuna cewa,
daga watan Janairun farkon wannan shekara zuwa tsakiyar wannan wata na Maris,
an kai hari a kan masallatai 32 a fadin kasar Amurka, daga ciki kuwa har da
kone masallatai 11 kurmus.
Rahoton ya ce idan aka kwatanta da farmakin da
masu kyamar musulmi suka kai a kan masallatai da cibiyoyin musulmi a kasar
Amurka a cikin shekarar 2016, hare-haren watanni uku na farkon wanann shekara
sun ninka har sau biyu, wanda hakan ke tababtar da karuwar tsanain nuna kiyayya
da kyama ga msuulmia kasar Amurka, tun bayan da Donald Trump ya dare kan
kujerar shugabancin kasar.