IQNA

Palastinawa Masu Yajin Cin Abinci A Gidajen Kason Isra'ila

23:52 - April 26, 2017
Lambar Labari: 3481441
Bangaren kasa da kasa, Marwan Barguthi daya daga cikin fitattun Palastinawa da ke tsare a gidan kason Isra'ila, ya aike da wasika zuwa ga majalisun dokokin na kasashen duniya, domin neman su mara baya ga fursunonin Palastinawa da ke neman hakkokinsu.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Shafin yada labarai na Gaza Now ya bayar da rahoton cewa a cikin wasikar, Marwar Barguthi ya bayyana cewa; sun shiga yajin cin abinci a gidajen kason Isra'ila, domin neman a kyautata yanayin rayuwarsu, da kuma kawo karshen takura da cin zarafin da Isra'ila ke yi wa dubban Palastinawa da take tsare da su a gidan kaso.

Ya ce suna kira ga 'yan majalisun dokoki na kasashen duniya, da hakan ya hada da majalisar kungiyar tarayyar turai, kan su bi kadun halin da Palastinawa suke ciki a gidajen kason Isra'ila.

Yanzu haka dai fursunonin Palastinawa 1500 ne karkashin jagorancin marwan Barguthi suka shiga yajin cin abinci a gidajen kason kason Isra'ila, domin tilasta mahukuntan Isra'ila da su saurari bukatunsu, musamman halin kunci da suke ciki a gidajen kaso.

3593191

captcha