Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na thisislancashire cewa, wannan cibiya da ke gudanar da ayyukan alkhairi, tana karbar tallafi daga musulmi domin bayarwa ga yara marassa lafiya da marassa karfi.
Daga cikin kayan da suke saye kuwa har kayan wasa da kuma abubuwan ci da yara suke bukata, gami da daukar nauyin sayen magungunasu ga wadanda suke kwance a asibiti suna bukatar agaji.
Islam Atcha daya daga cikin mambobin wannan wannan cibiya ya bayyana cewa, babbar manufarsu ita ce kara samar da yanayi na fahimtar juna atsakanin musulmi da sauran mabiya addinai, kuma wannan aiki da suke yi musulnci ne ya koyar da su yin hakan.
Daga karshe ya yi fatan alkhairi ga dukaknin musulmi da kuma fatan za a yi salla lafiya.