IQNA

Zanga-Zanga A Tunisia Domin Yin Allawadai Da Rufe Masallacin Aqsa

23:01 - July 22, 2017
Lambar Labari: 3481726
Banagaren kasa da kasa, an gudanar da gagarumar zanga-zanga a kasar Tunsia domin nuna goyon baya ga al'ummar palastinu da kuma masallacin Aqsa.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nkalto daga shafin yada labarai na tap cewa, al'ummar Tunisa suna gudanar da jerin gwano a birnin Tunis fadar mulkin kasar Tunisia domin la'antar gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila dangane da cin zarafin musulmin Palastinu da kuma keta alfamar wurare masu tsarki.

Wannan zanga-zanga wadda ta samu halartar dubban al'ummar kasar ta Tunisia ta mayar da hankali ne kan yadda gwamnatocin kasashen larabawa da sarakunansu suka yi gum da bakunansu a kan abin da yake faruwa a kan al'ummar palastinu da kuma masallaci mai alfarma.

Baya ga birnnin Tunis an gudanar da rin wanan babban jerin gwano a wasu biranan na kasar Tunisia a jiya, inda ake la'anatar gwamnatin yahudawan Isara'ila dangane da cin zarafin musulmi da ake yi a birnin Quds.

Tun a cikin shekara ta 1979 ce haramtacciyar kasar Isra'ila ta kwace iko da birnin Quds a hukumance, tare da mayar da masallacin Aqsa ai alfarm a matsayin wani da ke krkashin ikonsu, za su iya hana yin salla a cikinsa a duk lokacin da suka ga dama.

3621540


captcha