Sayyid Hassan Esmati shi ne shugaban ofishin, ya kuma gabatar da jawabi a lokacin bude taron bayar da horon, inda za a koyar da su ilmomin ahlul bait (AS) da kuma matsayinsu a cikin adinin muslunci.
A cikin bayanin nasa ya bayyana cewa, sun yi la'akari da yanayin hutun bazara ne da ake gudanarwa a wanann lokaci, wanda kuma za su yi amfani da wannan damar domin isar da sakon ahlul bait (AS) ga matasan wannan kasa ta msuulmi masu matukar son iyalan gidan manzon Allah.
Horon dai zai dauki tsawon kwanki 21 ana gudanar da shi, tare da hadin gwiwa da jami'ar Almustafa (SAW) a reshenta na kasar ta Senegal.