IQNA

Gargadi Kan Kisan Kiyashi A Kan Musulmin Afirka Ta Tsakiya

21:57 - August 23, 2017
Lambar Labari: 3481824
Bangaren kasa da kasa, Stephen O'Brien babban jami'in majalisar dinkin duniya kan ayyukan agaji ya bayyana cewa ga dukkanin alamu an yi kisan kiyashi a kan musulmi a Afirka ta tsakiya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, ya naklto daga jaridar Washington Post cewa, Stephen O'Brien babban jami'in majalisar dinkin duniya kan ayyukan agaji ya bayyana a ikin wani rahoton da ya shirya bayan gudanar da wata ziyara a jamhuriyar Afirka ta tsakiya, inda ya bayyana hakika an yi wa musulmi barna maras misiltuwa a kasar.

Stephen O'Brien ya kara da cewa, ya ziyarci yankuna da dama da aka fama da matsaloli na tsaro a kasar, inda ya ce jami'an sojin kasar sun tafka mummunan aikin kisan kiyashi a kan musulmi marassa rinjaye a kasar.

Inda ya ce a mafi yawan wuraren da ya ziyarta, ya samu cewa musulmi sun tsere sun bar dukkanin kaddarorinsu, yayin da sauran jama'a suke wawushe dukiyoyin msuulmi a gaban sojojin gwamnatin kasar, kamar yadda kuma sojojin sukan shiga gaba wajen kisan da ake yi wa musulmin.

Ya bayar da misalign birnin bangasu, inda ya ce an kasha daruruwan musulmi a hannun kungiyoyin masu adawa da musulmi da suke samun dauki daga dakarun kasar, kuma an kore dubban musulmi daga birnin, tare da wawushe dukkanin kaddarorinsu.

Babban jami'in na majalisar dinkin duniya ya ce wajibi ne a gudanar da bincike akn hakikanin abin da ya faru a jamhuriyar Afirka ta tsakiya, tare da gurfanar da dukkanin masu laifi a gaban kuliya.

3633763


captcha