Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a lokacin da take gabatar da wani jawabinta a gaban majalisar dokokin kasar Birtaniya, Warsi ta bayyana cewa abin takaici ne yadda wasu kafofin yada labarai a kasar suke taka rawa wajen yada kyamar musulmi a tsakanin al'ummar Birtaniya.
Ta ce wannan ba abu ne da za a lamunce da shi, domin kuwa babu wanda yake da hakkin ya tuhumi dukkanin musulmi da aikata ba daidai ba, kuma wadanda suke aikata ta'addanci da sunan musulunci, kaso mafi girma a cikin musulmi a duniya ba su goyon bayansu.
Daga karshe ta kirayi gwamnatin Birtaniya da ta sauke nauyin da ya rataya a kanta wajen kare rayukan musulmi da dukiyoyinsu, daga masu yi musu barazana a kasar.