Kamfanin dillancin labaran ma’a ya bayar da rahoton cewa, da jiffin safiyar yau ne wasu ‘yan bindga da ba a san ko su wane ne suka bude wutar bindiga a Sheikh Muhammad sa’ada a lokacin da yake fitowa daga masallacin Tauhid da yake limanci.
Jim kadan bayan faruwar lamarin an yi kokarin kai malamin asibiti, amma rai ya yi halinsa, jami’an tsaro sun iso wurin, kuma sun fara gudanar da bincike, amma babu wani mutum ko wata kungiya da ta dauki alhakin aikata wannan aika-aika.
Haka nan kuma daga bangaren jami’an tsaron babu wani bayani na kame wasu da ake zargin suna da hannua cikin lamarin.