IQNA

Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama 13 Sun Bukaci A Saki Fursunonin Siyasa A Bahrain

23:54 - April 07, 2018
Lambar Labari: 3482548
Bangaren kasa da kasa, Kungiyoyin kare hakkin bil-Adama 13 ne suka bukaci mahukuntan kasar Bahrain da su hanzarta sakin dukkanin fursunonin siyasa da ake tsare da su a kasar.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, A bayanin hadin gwiwa da kungiyoyin kare hakkin bil-Adama 13 suka fitar sun bukaci mahukuntan Bahrain da su hanzarta sakin fursunonin siyasa da ake tsare da su a gidajen kurkukun kasar musamman Abdul-Hadi Khawajah.

Tun a ranar tara ga watan Aprilun shekara ta 2011 ne jami'an tsaron kasar Bahrain suka kame Abdul-Hadi Khawajah fitaccen mai kare hakkokin bil-Adama da ke da izinin dan kasa a Denmark kan nuna rashin amincewarsa da jibge sojojin Saudiyya a cikin kasar Bahrain da nufin murkushe zanga-zangar lumana, inda kotu a Bahrain ta zartar da hukuncin daurin rai da rai a kansa. 

3703356

 

 

 

captcha