Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, an gudanar da taron girmama yaran ne a lardin sharqiyya na Masar.
Daga cikin yara akwai wadanda suka hardace rubuin kur’ani, akwai wadanda suka hardace juzui 30, kamar yadda kuma akwai wadanda sun kammala hardarsa baki daya.
Haka nan kuma an bayar da kyautuka da suka hada da shaidar kammala karatun kur’ani da kuma allunan girmamawa da kuma kudade.