IQNA

Jami’an Tsaro Sun Kame Daruruwan Masu Zanga-Zanga A Sudan

23:42 - January 08, 2019
Lambar Labari: 3483298
Bangaren kasa da kasa, ministan harkokin cikin gida na kasar Sudan ya bayyana cewa tun lokacinda aka fara tashe-tashen hankula na baya-bayan nan kasar Sudan an kama mutane.

Kmafanin dillancin labaran iqna, ya nakalto ministan cikin gida na kasar ta Sudan yana fadar haka a jiya Litinin. 

Ministan ya kara da cewa mutane sha tara ne suka rasa rayukansu tun lokacinda aka fara tashe-tashen hankulan a shekarar da ta gabata.

Amma majiyar kungiyar Amnesty International tana cewa an kashe mutane kimani arba’in a rahoton da ta tattara daga kafafe masu amince a kasar ta Sudan.

Tun ranar sha tara ga watan Decemban da ta gabata ce mutanen kasar sudan suka fara zanga-zangar yin alllawadai da karin farashin kayakin abinci musamman bredi a kasar. 

Mutanen kasar sudan dai suna bukatar shugaban Umar Hassan Albashir ya kawo karshen shugabancuin kasar da yake yi tun shekaru talatin da suka gabata.

A bisa tsarin mulkin kasar Sudan a halin yanzu dai shugaban zai kawo karshen mulkinsa a kasar ne a shekara mai zuwa.

3779088

 

 

 

captcha