Kamfanin dillancin labaran iqna, a lokacin da take zantawa da manema labarai jiya a birnin Bagadaza na kasar Iraki, babbar jami’ar majalisar dinkin duniya a Iraki bayan ganawarta da Ayatollah Sistani, Jeanine Hennis-Plasschaert ta bayyana cewa, Ayatollah Sayyid Ali Sistani ya mayarwa Trump da martini kan sukar kasar Iran da kuma neman sanya Iraki a cikin matsala.
Ta ce Ayatollah Sistani ya sheda mata cewa Trump ba shi da hakkin yin amfani da kasar Iraki domin cutar da wata kasa,kuma hakan ba a bu ne da al’ummar Iraki za su amince da shi ba.
Trump ya yi furucin cewa za su ci gaba da kasancewa a cikin kasar Iraki domin sanya ido akn kasar Iran, yana mai yin ishara dacewa sojojin Amurka da ke Iraki suna cikin kasar ne domin dakon Iran.