Kamfanin dillancin labaran iqna, ya bayar da rahoton cewa, da jijjifin safiyar yau Litinin Falastinawa 'yan gwagwarmaya sun harba wani makamai mai linzami daga yankin zirin gaza zuwa kusa da birnin Tel Aviv fadar mulkin haramtacciyar gwamnatin yahudawan Isra'ila.
Majiyoyin gwamnatin yahudawan sun ce makamain ya sauka a kan wani gina na yahudawa, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar 7 daga cikinsu.
A nasa bangaren Firayi ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu wanda ya nufi Amurka domin halartar bababn taron kungiyoyin yahudawa a Amurka, ya sha alwashin daukar mataki kan kungiyoyin gwagwarmayar falastinawa kan hakan.
Tun kwanaki uku da suka gabata ne jiragen yakin Isra'ila suke ta yin lugudan wuta akan gidajen Falastinawa a cikin zirin Gaza, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwa da kuma jikkatar mutane a yankin.