IQNA

Isra’ila Na Tsare Da ‘Yan Jarida 22 A Gidajen Kaso

23:58 - April 16, 2019
Lambar Labari: 3483552
Bnagaren kasa da kasa, gwamnatin Ira’ila tana tsare da ‘yan jarida 22 gidan kaso bisa laifin dauka rahotanni a wuraren da jami’an tsaro suke kai farmaki kan Falastinawa.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya abyar da rahoton cewa, Cibiyar kula da kare hakkokin ‘yan jarida ta Falastinu ta fitar da wani bayani a jiya, wanda a cikinsa take bayyana cewa, a halin yanz akwai ‘yan jarida 22 a gidan kason Isra’ila da ake tsare da su 3 daga cikinsu mata ne.

Bayanin y ace dukkanin wadannan ‘yan jarida babu wani wanda ya aikata wani laifi, abin da ake tuhumarsu shi ne suna daukar rahotanni tare da yada labarai kan hare-haren da da jami’an tsaro suke kai wa kan falastinawa a cikin gaza da kuma sauran yankunan gabar yamma da kogin Jordan da Quds.

Yanzu ahka dai an yanke hukuncia kan 7 daga cikinsu, 4 kuma babu hukunci, 11 uma suna jiran hukunci.

 

3804420

 

captcha