IQNA

Bayanin Dan Sheikh Zakzaky kan Mahaifinsa

22:53 - July 14, 2019
Lambar Labari: 3483839
Bangaren kasa da kasa, dan sheikh Ibrahim Zakzaky ya fitar da wani bayani dangane da yanayin da mahaifinsa yake ciki da kuma fatan sakinsa nan ba da jimawa ba.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Muhammad Ibrahim zakzaky ya rubuta cewa; Tun bayan rubutun da na yi a ranar bakwai ga watan Yulin dubu biyu da sha tara, wanda a cikinsa na zayyano irin matsanancin halin da mahaifana suke ciki; mashahurai a cikin gwamnatin nan sun tuntubi wasu daga Iyalinmu ciki har da ni.

Sun yi mana alkawarin cewa, za su ba mu damar yin abin da ya dace kan rashin lafiyan Mahaifana zuwa Asibitin Kasar waje. Tun bayan nan sun dauki matakan da suka dace wadanda muke ganin akwai alamun nasara. Duk da cewa, akwai sauran aiki da ya rage kan batun.

Bisa la’akari da irin gaggawar da lamarin ke buqata, wanda su ma sun fahimci haka; ina so na yi amfani da wannan dama wurin kiransu da su hanzarta musamman da aka fahimci cewa lokaci na ci gaba da Kurewa kan rashin lafiyan nasu.

Duk da har zuwa yanzu, jikin nasu ba wai ya yi dadi ba ne, sai dai kawai zan iya cewa akwai magana a kasa. Nan da ‘yan kwanaki zansake yin rubutu kan halin da a ke ciki.

Ko a yanzu da nake ganin an samu wani ci gaba wurin yin wani abu, amma ba zan yi sanyin jiki wurin ganin buqatar a gaggauta yin wani abu kan jikin na mahaifana ba; musamman ma ganin an kai su Asibiti.

Idan a ka ci gaba da samun wata natija irin wacce a ka samu a kwanaki biyu da suka gabata zan sanar; idan a ka samu tsaiko na babu dalili shi ma zan sanar; idan kuma a ka dakatar da maganar ma gabadaya shi ma dai za a ji daga gare ni.

3826938

 

captcha