Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Yeni Asya na kasar Turkiya cewa; An bude bangaren nazarin tauhi a cikin harshen turancin ingilishi a jami'ar Ankara da ke birnin Ankara na kasar Turkiya, wanda zai rika dauakar dalibai 'yan kasashen waje , wanda kuma bangaren zai fara bayar da karatu a cikin watan farkon shekarar miladiyya mai kamawa. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan shi ne karon farko da aka bude wani reshen nazarin tauhidi a jami'ar birnin Ankara da ma sauran jami'oin kasar Turkiya, wanda za a rika bayar da laccoci a cikin harshen turanci, wanda kuma zai rika daukar 'yan kasashen waje.
438302