IQNA

Zaman Taro Karo Na Biyu Tsakanin Mabiya Addinan Musulunci Da Buda A Qom

13:55 - April 20, 2011
Lambar Labari: 2109152
Bangaren kasa da sa, an kammala gudanar da wani zaman tattaunawa tsakanin addinai biyu na muslunci da kuma Buda, wanda shi ne karo na biyu da za a gudanar da irinsa a birnin qom da ke jamhuriyar muslunci ta Iran, tare da halartar masana daga dukkanin bangarorin mabiya addinan guda biyu.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo an bayyana cewa, an kammala gudanar da wani zaman tattaunawa tsakanin addinai biyu na muslunci da kuma Buda, wanda shi ne karo na biyu da za a gudanar da irinsa abirnin qom da ke jamhuriyar muslunci ta Iran, tare da halartar masana daga dukkanin bangarorin mabiya addinan guda biyu masu dadadden tarihi.
Addinin muslunci da kuma addinin Buda, dukkaninsu addinai da suke da manufa fahimtar juna tsakaninsu da sauran addinai, duk da irin banbancin akida ta addini da ke akwai tsakaninsu, amma sun hadu a kan wasu abubuwa na ‘yan adamtaka, wadanda suke da matukar muhimamnci a rayuwar dan adam ga abki daya.
An gudanar da wannan zaman tattaunawa tsakanin addinai biyu na muslunci da kuma Buda, wanda shi ne karo na biyu a birnin qom da ke jamhuriyar muslunci ta Iran, tare da halartar masana daga dukkanin bangarorin mabiya addinan guda biyu, kuma masana sun bayar da gudunmawarsu a taron.
776617

captcha