Kamfanin dillanicn labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Bawwabah News cewa, Nadiyah Mabruk babbar jami’a mai kula da shirin radiyo kur’an ta jagoranci bude taron.
Sheikh Muhammad Shaltut daya daga cikin ma nyan malamai kuma tsohon babban malamin cibiyar Azahar ya gabatar da jawabi, inda ya bayyana cewa an bude wanann gidan radiyo ne da muryar Sheikh Munshawi.
Nadiya Mabrk ta bayyana cewa, wannan gidan radiyo yana daya daga cikin gidajen radiyo na kasashen larabawa da suka fi jimawa, kuma daya daga cikin mawakan muslunci Mahmud Hassan Isma’il shi ne wanda ya fara da gabatar da wakokin muslunci a cikinsa.
An bude wannan radiyo ne a ranar 29 ga watan maris na shekara ta 1964, wanda kuma tun daga wannan lokacin ya samu babbar karbuwa a wajen al’ummar kasar Masar.