IQNA

Obama: Tsangwamar Musulmi Saboda Addininsu Ya Saba Wa Kai'da Da Doka Ta Amurka

23:36 - July 22, 2016
Lambar Labari: 3480637
Bangaren kasa da kasa, Shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana tsangwamar da wasu suke yi wa musulmi masu yin gudun hijira zuwa Amurka da cewa hakan ya saba wa dukkanin dokokin na kasar.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na Reuters ya bayar da rahoton cewa,a lokacin da yake gabatar da wani jawabi a jiya a fadar White House da ke birnin Washinton, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana cewa, musulmin kasar Amurka daidai yake da kowane dan kasar Amurka ba tare da wani banbanci ba, kuam babu wani dalili da zai sanya wasu su rika tsangwamar musulmi masu yin gudun hijira zuwa Amurka, domin kuwa tsangwamar mutum saboda addininsa saba wa doka a kasar Amurka.

Obama yana mayar da martani ne a fakaice a cikin bayanin nasa a kan Donald Trump dan takarar shugabancin Amurka a karkashin inuwar jam'iyyar Republican, wanda ya bayyana adawarsa karbar musulmi masu yin gudun hijira zuwa Amurka, inda yake bayyana hakan a matsayin bababn hadari na karuwar ta'addanci a kasar.

Gwamnatin barck Obama dai ta karbi dubban musulmi 'yan gudun hijira daga kasashe daban-daban, da hakan ya hada da dubban 'yan kasar Syria, da suka tsere wa yakin da aka haifar a kasarsu, lamarin ke ci gaba da fuskantar kakkausar suka daga masu kyamar musulmi, musamamn ma magoya bayan Donald Trump na jam'iyyar Republican.

3516810

captcha