A nasu bangaren mahukuntan kasar ta Sweden sun bayyana rashin jin dadi dangane da faruwar lamarin, a daidai lokacin da jami'an tsaro suka sanar da cewa sun shiga gudanar da bincike kan lamarin, da zimmar kame duk wadanda suke da hannu a cikin wannan aika aika, domin gurfanar da su a gaban kuliya.
Kimanin musulmi dubu 400 ne dai suke rayuwa a cikin kasar Sweden, kuma ba su cika fuskar matsaloli irin wadannan ba daga jama'ar gari, sai bayan da aka fara samun hare-haren ta'addanci daga 'yan takfiriyyah a cikin kasashen turai.