Donald Trump ya kara da cewa, duk da cewa maslahar Amurka ita ce a gaba a kan komai a wurinsa, amma kuma zai yi mu'amala tare da dukkanin kasashe na duniya bisa mutunci da girmama juna.
Kamar yadda ya ce kuma zai hada da kai tare da dukkanin mutanen Amurka ba tare da nuna banbanci na addini ko siyasa ko kabilanci ba, sabanin kalaman da aka saba ji daga bakinsa a lokutan baya.
A cikin watan Disamban shekarar 2015 da ta gabata ce, Trump ya bukaci da a hana musulmi shiga cikin kasar Amurka, tare da yin kira da a rika sanya ido a kan sauran musulmin da ke cikin kasar, tare da bincika masallatansu da wuraren ibadarsu.