Jabbar Al-his babban daraktan kamfanin zirga-zirgar jiragen kasa na kasar Iraki ya bayyana cewa, sun sanya dukkanin jiragensu da ke zirga-zirga a kasar da su mayar da hankali wajen daukar masu ziyarar arbaeen na Imam Hussain (AS).
Ya kara da cewa wannan abin da suke yi yana a matsayin hidima ga Imam Hussain da iyalan gidan manzon Allah, kuma aiki ne na lada.
Kamfanin jiragen kasa na kasar Iraki yana karbar wasu 'yan kudade daga masu ziyarar, kamar yadda yake bayar da dukkanin abubuwan bukata ga masu tafiya na abinci da sauransu.