IQNA

Kotun Manyan Laifuka Ta Duniya Ta Bukaci Najeriya Ta Yi Bayani kan kisan 'Yan Shi'a

20:37 - November 18, 2016
Lambar Labari: 3480952
Bangaren kasa da kasa, kotun ICC ta bukaci Gwamnatin Najeriya da ta yi mata bayyani kan kisan gillar da Sojoji suka yi wa Musulmi shekarar da ta gabata a kasar.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin All Africa cewa, bayan wannan wasika da Kotun ta aikewa Najeriya, Babban mai shara'a na kasar tare da Ministan shara'a sun isa birnin Hague na kasar Holland dake a matsayin cbiyar kotun domin kan kare Gwamnati kan kisan gillar da ta yi 'yan uwa musulmin almajiran sheikh zakzaky shekarar da ta gabata a birnin Zazzau.

A bangare guda, 'yan uwa musulmi almajiran shekh Ibrahim Yakubu Elzakzaky dake birnin Abuja sun gudanar da zanga-zanga a jiya Laraba domin nuna bacin rai da adawa kan kisan gillar da jami'an tsaron jihar Kano suka yiwa 'yan uwansu a yayin da suka tattaki na zagayowar ranar arabi'in din Imam Husain ranar Litinin din da ta gabata.

Mahalarta zanga-zangar sun tabbatar da cewa Jami'an tsaron Kanon sun hallaka 'yan uwa sama da dari tare kuma da da yin awan gaba da gawawwakinsu.a yayin da suka isa cibiyar kare hakin bil-adama ta kasar sun bukaci kungiyar da ta shaidawa Shugaban kasar cewa su ma 'yan kasa ne,dole a kare musu hakin su kamar ko wani dan kasa, bai dace ba a dinga kai musu hari a yayin da suke gudanar da addininsu.

3546688


captcha