Ya ci gaba da cewa tun daga lokacin da aka fara gudanar da tarukan na arbaeen daga makon da ya gabata, ya zuwa masu ziyara daga kasashen ketare miliyan uku da rabi ne suka isa birnin karbala, yayin da kuma fiye da Irakawa miliyan shida daga sassa na kasar suka isa birnin domin gudanar da tarukan na ziyarar arbaeen.
Haka nan kuma ya yi ishara da cewa, za a ci gaba da gudanar da ayyukan ziyarar ta arbaeen daga nan har zwa ranar Litinin, a kan ba zai yiwu a iya bayar da hakikanin alkalumma na krashe ba dangane da adadin masu ziyarar na ciki da wajen kasar Iraki ba.
Ya ce a halin yanzu za a iya cewa adadin masu shiga da fita birnin na Karbala ksan daya ne, domin a halin yanzu mutanen da suka yi ziyara suna fita ne, saboda babu wurin zama, garin ya gama cika makil da mutane.