Haka nan kuma ana gudanar da irin wadannan taruka a tsibirin Zanzibar a masallacin Alghadir, tare da halartar mabiya mazhabar iyalan gidan manzon Allah da ma sauran jama’a musulmi.
Rahoton ya kara da cewa bisa ga alada ana gudanar da irin wadanna taruka a masallacin yan Khoja, kuam acikin wadannan kwanaki taron yana samun halartar jama’a masu tarin yawa.
Za a ci gaba da gudanar da tarukan har zuwa karshen watan Safar, wanda zai hadu da lokacin tunawa da rasuwar ma’aiki (SAW) da kuma shahadar Imam Hasan Almujtaba (AS) da kuma shahadar Imam Ridha (AS).