Kamfanin dillancin labaran IQNA ya habarta cewa, Shafin yada labarai na Nigerian Bulletin ya bayar da rahoton cewa, gwamnatin jahar Lagos ta sake dawo batun hana dalibai saka hijabi a makarantu, inda ta mika batun ga kotun koli, bayan da wata kotun daukaka kara ta yi watsi da dokar, tare da bayyana hakan a matsayin tauye hakkokin dalibai mata musulmi.
Gwamnatin jahar Lagos dai ta fake ne batun matsalar tsaro a arewa maso gabashin Najeriya, inda take bayyana cewa saka hijabi a makarantu zai iya zama barazana ta fuskar tsaro.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama da dama a Lagos da kuma kungiyoyin mata musulmi sun kakkausar suka dangane da wannan mataki na gwamnatin jahar, tare da shan alawashin bin dukkanin hanyoyi na shari'a domin kalubalantar wannan doka.