IQNA

Wata Tawagar Iran Ta Halarci Wani Shiri Na Kur'ani A Senegal

22:30 - December 17, 2017
Lambar Labari: 3482209
Bangaren kasa da kasa, wata tawagar Iraniya makaranta kur'ani sun isa kasar Senegal domin halartar wani taron kur'ani mai tsarki.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na bangaren hulda da jama'a na cibiyar yada al'adun muslunci cewa,tawagar Mi'ad daga yankin Ahwaz ta halarci wani taron kur'ani da aka shirya  a Senegal.

Wannan taron dai an shirya  shi ne domin gabatar da karatun kur'ani da wakokin bege ga manzon Allah wanda, wanda cibiyar Nabiyullah ta shirya, kuma ta gayyaci kungiyar Mi'ad daga Iran.

Taron dai an gudanar da shia  daren jiya, tare da halartar malamai da kuma masana, gami da makaranta kur'ani, kamar yadda kuma wasu daga cikin larabawa mazauna birnin Dakar suka halrci gami da jami'ar Almustafa (SAW) a reshenta da ke kasar ta Senegal.

Taron dai ya samu karbuwa daga mutane da daman a kasar Senegal.

3673388

 

captcha