Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kafofin yada yada labaran Palestine sun bayar da rahotanni da ke cewa,a yau da ran atsaka jami'an tsaron Haramtacciyar kasar Isra'ila da suka hada da sojoji da kuma 'yan sanda, sun kutsa kai a cikin garin Kilkiliya, inda suka rufe babbar mashigar garin.
Bayan shigar su sun yi ta bincike a cikin gidajen palastinawa mazauna garin, kamar yadda kuma suka kame wasu matasa suka yi awon gaba da su.
Haka nan kuma sun yi ta antaya hayaki mai sanya ahawayea ko'ina a cikin unguwanni, lamarin da ya sanya mata da kanan yara suka yi shakewa, kamar yadda kuma suka yi ta tarwatsa yara a lokacin da suke tashi daga makarantunsu.