Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar Dail Nation ta kasar Kenya ta habarta cewa, an gudana da gasar ne albarkacin watan Ramadan.
A bangaren harda na gasar an samu halartar mahardata daga kasashen Keya, Tanzania, Aljeria, Komoros, Burundi, Rwanda, Congo, Malawi.
An watsa gasar kai tsaye a gidajen talabijin na kasa Tanzania, tare da halartar manyan malamai da jami’ai da kuma firayi minister wanda ya halarci taron rufe gasar.
Wanda ya nasara a gasar ya samu kyautar kudi shilling dubu 45, kamar yadda kuma ya samu kyautukan na daban da ban a kudade ba.