Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a cikin wannan wata na Ramadan an fara gudanar da wani shiri na koyar da matasan musulmi a Myanmar ilmomin addinin musulunci domin samun masaniya kan addini.
Daga cikin abubuwan da ake koyar da su, har sanin hukuncin salla da sauran ayyukan ibada da suka hada da azumi da sauransu.
Mirza Gholam Abbas, Muhammad Rafi, Muhammad Zahed, Muhammad Abbas Nasrullah na daga cikin malaman da ke bayar da horon.