Kamfanin dillancin laraban iqna ya habarta cewa, Assad wanda ke bayyana hakan a wata hira da tashr talabijin ta Rasha ya ce zamu iya yin amfani da karfi don kwato yankunan dake karkashin mayakan a yankin arewa maso gabashin kasar.
Shugaba Assad ya kuma ce a shirye yake ya tattauna da mayakan na FDS, amma idan hakan ya cutura, to zamu tsarkake yankunan da karfi.
A hannu daya kuma shugaban Siriyar ya ce, saura kiris a fafata tsakanin tsakanin dakarun Amurka dana Rasha a kasarsa, saidai an sa'ar kauce wa hakan.