Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, talabijin na masirah ya watsa rahoton cewa, Jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun yi luguden wuta kan gidajen jama'a a yankin Al-Hajlah da ke lardin Sa'adah a shiyar arewacin kasar Yamen. Kamar yadda suka kai jerin hare-haren kan yankin Al-Zubaid da ke lardin Hudaidah da ke yammacin kasar.
A kwanakin baya ma jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun kai wasu munanan hare-haren wuce gona da iri kan asibitin Al-Saurah da kasuwar sayar da kifaye a garin Hudaidah, inda suka kashe mutane fiye da sattin tare da jikkata wasu kimanindai na daban.