Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Tashar Lu'ulu'a ta bayar da rahoton cewa, a jiya tawagar likitoci masu kula da lamarin lafiyar Ayatollah Sheikh Isa Kasim sun sanar da cewa, an sallami malamin daga asibiti, inda yanzu haka yake zaune a wani wuri a birnin London, kuma zai ci gaba da zuwa asibitin lokaci zuwa lokaci domin duba lafiyarsa.
Masarautar mulkin kama karya ta kasar Bahrain ta tsare Sheikh Isa Kasim a cikin gidansa har tsawon kusan shekaru biyu duk kuwa da rashin lafiyar da yake fama da ita, amma daga karshe sakamakon matsin lambar duniya, ta bari an fitar da shi zuwa asibiti a London.
Masarautar kama karya ta kasar Bahrain ta zargin malamin da goyon bayan masu fafutukar neman hakkokinsu da aka haramta musu a matsayinsu na 'yan kasa a kasar ta Bahrain.