Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, tun a daren jiya ne aka fara shirin gudanar da tarukar Ghadir a birnin Najaf Ashraf inda hubbaren Imam Ali (AS) yake.
Dubban daruruwan musulmi mabiya mazhabar iyalan gidan manzon Allah ne suka halarci wurin wannan taro.
An gudanar da jawabai kan matsayin wannan rana da kuma irin darusan da take tattare da su ga dukkanin al’ummar musulmi, kasantuwar wannan rana ita ce ranar cikar addinin Alah madaukakin sarki.