IQNA

A Masar An Kashe Kiristoci 7 A Wani Harin Ta'addanci

23:59 - November 02, 2018
Lambar Labari: 3483093
Bangaren kasa da kasa, Rahotanni da suke fitowa daga Masar sun ce wasu 'yan bindiga ne su ka kai hari akan motar safa da take dauke da kirisitoci kibdawa.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Bakwai daga cikin mutanen sun mutu sai kuma wasu 14 da su ka jikkata.

Tashar talabijin din al-Mayadeen ta ambato limanin kiristoci kibdawa na yankin Minya yana cewa; An kai wa mutanen hari a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa gundumar Suhaj.

Kamfanin dillancin labarun Reuters kuwa ya ce an kai harin ne a kusa da majami'ar Saint Samuel da take a gundumar Minya.

Kawo ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan wadanda su ka kai harin da kuma manufarsu.

A cikin shekaru biyu na bayan nan an kai irin wannan harin akan mabiya addinin kirista a cikin kasar ta Masar wanda ya ci rayukan fiye da mutane dari.

Masar na fama da matsalar ta'addanci da kungiyoyi masu dauke da makamai suke kai hare-hare.

3760576

 

 

 

 

 

captcha