Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a yau kotun masarautar mulkin kama karya ta kasar Bahrain ta yanke hukuncin daurin rai da rai a kan shugaban jam’iyyar Alwifaq mai adawa a kasar sheikh Ali Salman, da Hassan Sultan dakuma Al Aswad.
Kafin wannan lokacin da kotun kolin kasar ta bayar da bayani kan rashin sahihancin dukkanin zarge-zargen da masarautar mulkin kma karya ta Bahrain take yi a kan wadannan mutane masu neman gyara ta hanyar lumana akasar.