IQNA

‘Yan Adawa A Sudan Sun Sha Alwashi Ci Gaba Da Zanga-Zanga

21:25 - April 23, 2019
Lambar Labari: 3483572
Masu adawa da hambararrar gwamnatin kasar Sudan, sun sha alwashin gaba da gudanar da zanga-zanga har sai an mika mulki ga farar hula.

Kamfanin dillancin labaran iqna, ya nakalto rahoto daga reuters cewa, majalisar sojoji da ke tafiyar da mulki a kasar Sudan ta kasa shawo kan ‘yan adawa domin samu daidaito kan batun mika mulki.

Majalisar sojojin ta bayyana ci gaba da gudanar da zanga-zanga da gangami da ‘yan adawa suke yi da cewa ba zai taimaka ba wajen warware matsalar da kasar ta samu kanta  a ciki.

Bayanin majalisar sojin ya yi nuni da cewa; akwai bukatar a zauna a fahimci juna tsakanin majalisar sojin da kuma sauran dukkanin bangarori na siyasa da na al’umma, domin samun daidaiton baki kan yadda za a mika mulki ga farar hula, da kuma hanyoyin da za a bi kafin kaiwa ga hakan.

Sai dai a nasu bangaren bangarorin adawa sun yi watsi da wannan kira, inda suke jaddada bukatar su ga sojojin das u mika mulki ga gwamnatin rikon kwarya ta farar hula, wadda za ta shirya sahihin zabe na dimukradiyya a kasar.

3805766

 

 

 

 

 

 

captcha