IQNA

Hizbullah ta Kakkabo Jirgin leken Asirin Isra’ila

17:42 - September 09, 2019
Lambar Labari: 3484034
Bangaren kasa da kasa, Mayakan kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon sun harbo jirgin yaki maras matuki na Isra’ila.

Kamfanin dilalncin labaran iqna, shafin yada labarai al-ahad ya bayar da rahoton cewa, a wata sanarwa da kungiyar gwagwarmayar musuluncin ta Hizbullah ta fitar dazu, ta ce; An yi amfani da makamin da ya dace wajen harbo jirgin saman maras matuki na Isra’ila a garin “Ramiyah”

Sanarwar ta ci gaba da cewa; Bayan harbo jirgin saman maras matuki, ‘yan gwagwarmayar sun dauke shi yana hannunsu.

Tun bayan harin da Isra’ila ta kai da jirgi sama maras matuki a unguwar Dhahiya dake cikin birnin Beirut, babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah Sayyid Nasarllah ya bayyana cewa; Daga yanzu kungiyar za ta rika harbo jiragen sama maras matuki na Isra’ila.

3841136

 

captcha