Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Palestine cewa, a cikin wani jawabinsa a yau, Netanyahu ya bayyana cewa; bayan kammala zaben Knesset da ‘yan kwanaki Amurka za ta gabatar da shirinta na yarjejeniyar karni.
Netanyahu ya ce ya nada shugaban ofishinsa domin ya jagoranci shirin mamaye yankunan falastinawa na Agwar da har zuwa dead sea.
Ya kara da cewa, mayar da yankunan gabar yamma da kogin Jordan da kuma Agwar na da matukar muhimmanci ga makomar tsaron Isra’ila, a kan haka wannan zai zama daya daga cikin bangarori na yarjejeniyar karni.