Kamfanin dillancin labaran iqna, majiyoyin labaran kasar Saudiya sun sanar da tashin gobara a tashar jiragen birnin jeddah, tare da bayyana cewa har yanzu ba a kai ga gane musabbabin tashin gobarar ba.
Jaridar Sabak ta kasar Saudiya ta ce an dakatar da duk wani kai kawo na jiragen kasa a wannan tasha, tare kuma da kwashe dukkanin fasinjoji da ma'aikatar tashar ganin yadda gobarar ke kara ruruwa.
A nata bangare tashar talabijin din Al-arabiya ta sanar da cewa babu wani mutun da ya rasa ransa ko kuma ya jikkata sanadiyar tashin gobarar.