IQNA

Gwamnan Najaf: An Kame Wasu Na Hankoron Kashe Malamai A Najaf

22:10 - October 04, 2019
Lambar Labari: 3484118
Bangaren kasa da kasa, Lui Alyasiri gwamnan Lardin Najaf a Iraki ya bayyana cewa, an kame wasu na shirin cutar da manyan malaman kasara Najaf.

Kamfanin dillancin labaran iqna, tashar Almayadeen ta bayar da rahoton cewa, Lui Alyasiri gwamnan Lardin Najaf a Iraki ya bayyana cewa, an kame wasu na shirin cutar da manyan malaman kasar a birnin na Najaf.

Gwamnan na najaf ya kara da cewa dukkanin mutanen an kame su a lokacin da suka kutsa kaia  cikin unguwannin tsohowar Najaf, ida dukkanin manyan malaman addini na kasar Iraki suke, kuma mutanen suna da wani mummunan kudiri a kan malaman.

Wannan da an zuwa ne a daidai lokacin da wasu daga cikin mutanen Iraki suke zanga-zanga a wasu biranan kudancin kasar, suna korafi kan matsalolin rayuwa, musamman matsalolin rashin ayyukan yi a tsakanin matasa.

 

3847139

 

 

 

 

captcha