IQNA

Littafi Mai Suna Zama Musulmi A Birtaniya

20:57 - November 19, 2019
Lambar Labari: 3484256
Bangaren kasa da kasa, za a kaddamar da wani littafi mai suna zama musulmi a kasar Birtaniya.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, shafin cibiyar kare hakkin musulmi ta kasar Birtaniya ya bayar da rahoton cewa, ana shirin kaddamar da wani littafi na Mamnun Khan mai suna zama musulmi a kasar Birtaniya a ranar Alhamis mai zuwa.

Wannan lttafi dai ya kunshi bayanai dangane da yadda addadin musulmi yake karuwa  akasar, inda ake has ashen cewa daga kashi 5% zai kai kashi 10% daga zuwa shekara ta 2050.

Mamnun Khan dai ya karbi diri na uku a jami’ar Cambridge ta kasar Birtaniya, kuma yana yin nazari kan yanayin bunkasar addadin musulmi a kasar ta Birtaniya, inda ya gano cewa kimanin kashi hamsin na musulmin Birtaniya  akasar a aka hafe su, kuma adadin musulmin kasar zai ninka daga nan zuwa shekaru talatin.

3858206

 

 

 

 

 

 

captcha