IQNA

Tsayin Dakan Al’ummar Yemen A Gaban Masu Shishigi Hakan Abin Alfahari Ne

17:22 - November 20, 2019
1
Lambar Labari: 3484258
Shugaba Rauhani ya bayyana tsayin dakan da al’ummar Yemen suka yia  gaban masu girman kai da cewa abin alfahari ne ga al’ummar musulmi.

Kamfanin dillancin labaran iqna, shugaba Hassan Rauhani ya ci gaba da cewa” Nauyi ne na addini da ya rataya a wuyan Iran ta kasance tare da al’ummar Yemen domin kalubalantar hare-haren da ake kai musu, haka nan kuma a lokacin da suke tattaunawar sulhu.

Shugaban Rauhani wanda ya gana da sabon jakadan kasar Yemen a Iran, Muhammad Muhammad al-Deilami ya jinjinawa tsayin dakar al’ummar Yemen wajen fuskantar wasu wuce gona da iri.

Dr. Hassan Rauhani ya kuma ce; Babu kokonto akan cewa a karshe tsayin dakar al’ummar Yemen zai kai ga samun nasara akan makiya.

A nashi gefen, sabon jakadan kasar ta Yemen a Iran Muhammad Muhammad al-Deilami ya ce; Kasarsa tana son bunkasa alakarta da Iran a fagage da dama. Har ila yau ya ce; Al’umar Yemen ba za su taba mancewa da irin taimakon da jamhuriyar musulunci ta Iran ta yi musu ba.”

Tun a cikin watan Ogusta ne dai kasar ta Yemen ta ayyana sabon jakadanta a Iran wanda ya mika takardun kama aikinsa ga ministan harkokin wajen Iran Muhammad Jawad Zarif a farkon watan Satumba.

 

 

3858146

 

 

 

 

Wanda Aka Watsa: 1
Ana Cikin Dubawa: 0
Ba A Iya Watsa Shi: 0
Ba A San Shi Ba
0
0
ALLAH ANNABI YAKARAWA ANNABI DARAJA
captcha